in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bai kamata Amurka ta soki kasar Sin sakamakon wasu jita-jita ba, a cewar kakakin kasar Sin
2014-02-07 20:47:07 cri
Kwanan baya, a wurare daban daban ne wasu jami'an kasar Amurka suka ambaci shirin kasar Sin na shata sassan tsaron sararin sama a tekun Kudu, wanda a ganinsu mataki ne da kasar Sin ta dauka domin ta da zaune-tsaye, kuma zai haifar da rashin kwanciyar hankali a yankin da Sin ke ciki.

Dangane da lamarin, Hong Lei, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana a yau ranar Jumma'a 7 ga wata a taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan Beijing cewa, jami'an Amurka sun soki kasar Sin ne sakamakon wasu jita-jitan da masu tsattsauran ra'ayi na kasar Japan suka baza, na cewa, wai kasar Sin ta yi shirin shata sassan tsaron sararin sama a tekun Kudu. Don haka yadda jami'an ba su tabbatar da jita-jitan ba ya nuna cewa, ba su sauke nauyin da ya kamata su sauke ba.

Hong Lei ya kuma sake jaddada cewa, a matsayinta na wata kasa mai ikon mulkin kasa, kasar Sin na da ikon daukar dukkan matakan da suka wajaba domin tabbatar da tsaronta a sararin sama, ciki had da shata sassan tsaron sararin sama, abin da ya sa bai kamata a yi soki lamarin ba.(Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China