in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude taron shugabannin kungiyar AU karo na 22
2014-01-31 17:07:03 cri
An bude taron shugabannin kungiyar tarayyar kasashen Afirka karo na 22 mai taken "raya ayyukan noma da kuma samar da isashen abinci" a babban birnin kasar Habasha, Addis Ababa a ran 30 ga wata. Shugabanni, manyan jami'an gwamnati da kuma wakilai daga mambobin kasashen kungiyar AU sama da guda 50 sun tattauna kan harkokin raya ayyukan noman kasashen Afirka, samar da isashen abinci, yanayin tsaro, shirin menan bunkasuwar yankin da dai sauransu a yayin wannan taro na kwanaki biyu.

Tsohon shugaban kungiyar AU na wannan zagaye, firaministan kasar Habasha Hailemariam Dessalegn ya ba da wani jawabi a yayin bikin bude taron, inda ya nuna yabo ga sakamakon da nahiyar Afirka ta samu dangane da gudanar da shirin raya ayyukan noma na kasashen Afirka bisa dukkan fannoni cikin shekaru goma da suka gabata. A sa'i daya kuma, ya bayyana cewa, ya kamata kasashen Afirka su dukufa tare wajen shimfida zaman lafiya da na karko a kasar Sudan ta Kudu da kuma kasar Afirka ta Tsakiya, kada rikice-rikice na wasu kananan yankuna ya bata yanayin tsaron nahiyar Afirka gaba daya.

Shugabar hukumar zartaswar kungiyar AU Dlamini Zuma ta kuma ba da wani jawabi inda ta nuna fatanta ga nahiyar Afirka a shekarar 2063, da kuma aniyarta wajen cimma wannan burin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China