in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babbar jami'iyar AU ta yi kira ga bangarori daban daban na Masar da su yi hakuri su fara tattaunawa tsakaninsu cikin hanzari
2013-08-18 16:41:15 cri
Shugabar kwamitin kula da harkokin kungiyar tarayyar Afirka AU Madam Dlamini Zuma a jiya Asabar 17 ga wata ta yi kira ga bangarori daban daban na kasar Masar da su yi iyakacin kokarinsu da yin hakuri da juna, kana su kaddamar da tattaunawa a tsakaninsu cikin hanzari.

Madam Zuma ta yi wannan kira ne yayin da take halartar taron koli karo na 33 na kungiyar raya kudancin Afirka, wato SADC a birnin Lilongwe, hedkwatar mulkin kasar Malawi.

Ta bayyana cewa, kungiyar AU na nuna kulawa sosai kan batun tashin hankali da zubar da jini da ke faruwa a kasar Masar. Kana ta yi kira ga bangarori daban daban na kasar da suyi hakuri, su kuma kaddamar da tattaunawa a tsakaninsu cikin hanzari domin samun sulhu.

Haka zakila, Madam Zuma ta ce, kungiyar AU ta riga ta tura wata kungiyar kwararru ta babban mataki zuwa Masar. Idan ba za a iya kwantar da kurar da ta tashi a kasar ba, to kungiyar AU za ta duba yiwuwar kiran taron musamman na kwamitin kula da zaman lafiya da tsaro domin tattaunawa kan batun sa hannu cikin halin da Masar ke ciki.

Tun daga 14 ga wata ne, sojoji da 'yan sanda na kasar Masar suka fara korar masu zanga-zanga masu goyon bayan Mahammad Morsy a wasu filaye biyu da ke birnin Alkahira, lamarin da ya haddasa abkuwar rikice-rikice a wurare da dama a duk fadin kasar, wadanda suka yi sanadiyyar mutuwa da jikkatar da mutane masu dimbin yawa.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China