in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta bukaci kotun hukunta manyan laifukan duniya da ta jinkirta yanke hukunci ga shugabannin Kenya
2013-10-13 17:19:11 cri
Ranar 12 ga wata, an kammala taron musamman na kungiyar AU a birnin Addis Ababa, hedkwatar kasar Habasha na tsawon kwanaki biyu, shugabanni mahalarta taron sun cimma matsaya guda bayan yin shawarwari tsakaninsu, inda suka bukaci kotun hukunta manyan laifukan duniya da ta jinkirta yanke hukunci ga shugabannin Kenya, a kokarin kauracewa kawo illa ga zaman lafiya da tsaro da kwanciyar hankali a kasar.

A gun bikin rufe taron, shugaban kungiyar AU a wannan karo, kana firaministan Habasha Hailemariam Dessalegn ya yi jawabi cewa, a wannan taro, kasashe mahalarta taron sun cimma matsaya daya, inda suka bukaci kotun hukunta manyan laifukan duniya da ta yi taka-tsamtsam da kuma sauraron muryar kasashen Afirka, kuma ta bi ka'idojin duniya, wato kada ta yanke hukunci ga shugabannin kasa dake kan mulki. Ya ce, a kokarin kiyaye kundin tsarin mulki, da tabbatar da zaman lafiya da ikon mulkin kasa, kungiyar AU tana ganin cewa, bai kamata wata kotun kasa da kasa ta gurfanar da shugabannin kasashe membobin kungiyar AU dake kan mulki a gaban kotu ko kuma ci gaba da yanke hukunci kansu ba.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China