in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi kira da a yi kokarin rage bambancin da ke tsakanin yara a sassa daban daban na duniya
2014-01-31 17:06:26 cri
Ranar Alhamis 30 ga wata ne asusun kula da kananan yara na MDD wato UNICEF ya kaddamar da wani rahoton alkaluma na shekarar 2014 game da halin da yara suke ciki, inda ya yi kira ga kasashen duniya da su kara yin kokari da kirkire-kirkire wajen warware bambance-bambancen da ke tsakanin kananan yara a sassa daban daban na duniya.

Rahoton ya ce, alkaluman za su taimakawa gwamnatocin kasa da kasa wajen yanke shawara da daukar matakai, ta yadda za a ceci miliyoyin kananan yara da kuma kyautata zaman rayuwarsu.

Rahoton ya kara da cewa, tun bayan da aka kaddamar da yarjejeniyar kiyaye hakkokin kananan yara a shekarar 1989 zuwa yanzu, kasashen duniya sun samu babban ci gaba wajen kyautata halin da yara suke ciki, yayin da suke kokarin tabbatar da manufar bunkasuwa ta MDGs a shekarar 2015.

A sa'i daya kuma, rahoton ya nuna cewa, ya zuwa yanzu ana keta hakkokin kananan yara a wasu sassan duniya, haka kuma, alkaluman sun tono matsalar rashin adalci da kuma bambance-bambance iri daban daban da ake fuskanta a halin yanzu. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China