in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakataren harkokin wajen kasar Amurka ya gabatar da sabon shirin samar da zaman lafiya tsakanin Falesdinu da Isra'ila
2013-12-06 17:04:58 cri
A ranar 5 ga wata, sakataren harkokin wajen kasar Amurka John Kerry ya sake ziyarar Isra'ila da Falesdinu, inda ya gabatar da sabon shirin samar da zaman lafiya ga shugabannin bangarorin biyu, a yunkurin sa kaimi ga yin shawarwari a tsakanin Falesdinu da Isra'ila da ya samu tsaiko a kwanan baya.

Kerry da mashawarcinsa na musamman John R. Allen da daidai ne suka gana da firaministan kasar Isra'ila Benjamin Netanyahu da shugaban Falesdinu Mahmoud Abbas a birnin Kudus da Ramallah, kuma sun bayyyana sabon shirin samar da zaman lafiya gare su, wanda ya kunshi musayar yankunan kasa da batun hedkwatoci na kasashen biyu da sauransu.

Tuni, a wannan rana, wasu jami'an gwamnatin Isra'ila ciki har da Netanyahu suka fada wa kafofin yada labaru cewa, Isra'ila na bukatar tsaron kanta, kuma ba za ta yi sassauci game da batun tsaro a lokacin shawarwarin ba.

Bisa labarin da aka bayar, an ce. Isra'ila za ta tsaya tsayin daka game da kasancewar sojojinta a iyakokin dake tsakaninta da kasar Jordan, don ba da tabbaci ga tsaron iyakokin kasar, kuma tana fatan kafa wuraren tsinkaya a wasu yankunan yammacin gabar kogin Jordan.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China