in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin kasar Sin ya bukaci da a ingiza ci gaban shawarwari tsakanin Falesdinu da Isra'ila
2013-10-23 14:58:37 cri
A ranar 22 ga wata, mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin a M.D.D. Wang Min, ya yi kira ga Falesdinu da Isra'ila da su yi amfani da damar da ke gabansu, wajen ingiza ci gaban shawarwarin dake tsakaninsu.

Wang Min, wanda ya bayyana hakan a gun taron muhawara game da batun Gabas ta tsakiya, da kwamitin sulhu na M.D.D. ya shirya, ya ce kasar Sin kullum tana dauka cewa, ya kamata Falesdinu da Isra'ila su yi shawarwari a tsakaninsu don cimma burin kafa kasar Falesdinu mai cikakken ikon cin gashin kan ta, kuma mai hedkwata a gabashin birnin Kudus, bisa kuma iyakokin da aka shata a tsakaninta da Isra'ila a shekarar 1967, da tabbatar da zaman tare cikin lumana tsakanin kasashen biyu.

Ya ce, hakan na iya samuwa muddin aka nuna biyayya ga kudurorin da abin ya shafa na M.D.D., da ka'idar "mai da yankunan kasa domin samun zaman lafiya", da "shawarar wanzar da zaman lafiya ta kasashen Larabawa", da kuma "tsarin taswirar" shimfida zaman lafiya a yankin Gabas ta tsakiya.

Wang Min ya kara da cewa, kasar Sin tana fatan yin kokari tare da kasashen duniya, don ba da gudummawa wajen warware batun Falesdinu daga dukkan fannoni kuma cikin adalci, da samun dauwamammen zaman lafiya a yankin Gabas ta tsakiya.

Ya ce, yanzu, aikin farfado da shawarwari kai tsaye tsakanin Falesdinu da Isra'ila, da yunkurin samar da zaman lafiya a yankin Gabas ta tsakiya na samun gagarumin goyon baya, ya kuma yi fatan Falesdinu da Isra'ila za su yi amfani da wannan dama, wajen yin hadin gwiwa, don hana tabarbarewar yunkurin samar da zaman lafiya a tsakaninsu, tare da fatan za su gaggauta samun ci gaba a shawarwarin da suke gudanarwa.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China