in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta samar da dallar Amurka miliyan 86 don gudanar da taimakon jin kai a kasashe goma
2014-01-18 16:57:55 cri
A ran 17 ga wata, MDD ta sanar da samar da dallar Amurka miliyan 86 don taimakawa kasashen nan 10 dake fama da rikice-rikice da suka hada da kasashen Sudan, Yemen, Mali da dai sauransu.

Mataimakiyar babban sakatare mai kula da harkokin jin kai ta MDD Valerie Amos ta bayyana cewa, ko da yake wasu al'ummomin kasa da kasa na fama da rikicin jin kai mai tsanani a halin yanzu, ba za a iya samar da taimakon jin kai ga wadannan mutane yadda ya kamata ba. Kudin da MDD ta samar, za ta taimaka wa miliyoyin mutanen da ke fama da rikice-rikice ne, ba wai warware musu dukkan bukatunsu ba.

Bisa shirin MDD, kudin da za a baiwa kasar Sudan zai kai dallar Amurka miliyan 20, yayin da kasar Yemen za ta samu dallar Amurka miliyan 14, kasar Mali za ta samu dallar Amurka miliyan 11.5, kasar Chadi za ta samu dallar Amurka miliyan 10, kasar Colombia za ta samu dallar Amurka miliyan 4.5, kasar Djibouti za ta samu dallar Amurka miliyan 4, kasar Koriya ta Arewa za ta samu dallar Amurka miliyan 6.5, kasar Haiti za ta samu dallar Amurka miliyan 6, kasar Myamar za ta samu dallar Amurka 5.5, yayin da kasar Uganda za ta samu dallar Amurka miliyan 4. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China