in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata gamayyar kasa da kasa su sa ido kan kasar Japan
2014-01-14 20:56:48 cri
Kwanan baya, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya rubuta wani sharhi a jaridar " New Europe" ta kungiyar tarayyar kasashen Turai mai taken "bunkasuwar kasar Sin za ta tallafa wa kasa da kasa", inda ya bayyana cewa, a halin yanzu, wasu shugabannin kasar Japan suna kokarin karyata tarihi, lamarin da zai kawo barazana ga kasar, don haka, ya kamata gamayyar kasa da kasa su sa ido kan lamarin, don yin adalci ga bil Adam da kuma tsarin kasa da kasa bayan yakin duniya.

Cikin wannan sharhi, Wang Yi ya bayyana cewa, ra'ayin kasar Japan kan tarihinta na yakin da bai cancanta ba ya sha bamban da ra'ayin kasashen Turai kan yakin Nazi, wanda kasar Germany ta dauki alhakin laifin yakin da ta aikata.

Ya ce, kasar Sin za ta ci gaba da neman bunkasuwarta ta hanyoyin zaman lafiya, hadin gwiwa da kuma cimma moriyar juna, kuma za ta ci gaba da ba da gudummawa cikin harkokin kasa da kasa yadda ya kamata a matsayin wata babbar kasa, a sa'i daya kuma za ta kiyaye dangantakar abokantaka dake tsakaninta da kasashe makwabtaka kamar yadda ta saba yi. Wannan shi ne alkawarin da kasar Sin ta yi wa kasa da kasa kuma ba zai canja ba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China