in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen kasar Sin zai kai ziyara Afirka
2014-01-02 20:36:23 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Qin Gang, ya bayyana yayin taron manema labarai a yau Alhamis a nan birnin Beijing cewa, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi zai ziyarci kasashen Habasha, Ghana, Djibouti da Senegal daga ranar 6 zuwa 11 ga watan Janairu.

Qin Gang ya ce zabar kasashen Afirka da ministan ya yi don kai ziyararsa ta farko a sabuwar shekara, ya nuna yadda kasar Sin ke daukar Afirka da muhimmanci.

Ya ce, ya kasance al'ada ga ministocin harkokin wajen kasar Sin tun a shekara ta 1991, su fara ziyartar kasashen Afirka a kowace sabuwar shekara, kuma wannan ita ce ziyara ta farko da sabon ministan harkokin wajen kasar ta Sin ya kai kasashen Afirka da ke kudu da hamadar sahara, tun lokacin da sabbin shugabannin kasar suka kama aiki.

Mr Qin Gang, ya ce kasar Sin ta yi imanin cewa, ziyarar za ta kara zurfafa dangantakar abokanta, mutunta juna da hadin gwiwa da ke tsakanin kasashen biyu. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China