in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta nace wajen bin hanyar raya hakikanin hadin gwiwa tsakaninta da kasashen Afrika cikin daidaito kuma bisa sahihiyar zuciya
2014-01-07 11:02:10 cri
A ranar 6 ga wata, a gun taron manema labaru da aka shirya bayan da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gana da takwaransa na kasar Habasha Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya jaddada cewa, kullum kasar Sin ta kan nacewa ga bin hanyar raya hakikanin hadin gwiwa tsakaninta da kasashen Afrika cikin daidaito da amana kuma bisa sahihiyar zuciya.

Wang Yi ya furta cewa, dukkan kasashen Afrika, mambobi kasashen duniya ne, kuma suna da hakkin raya kansu, kuma akwai makoma mai haske wajen raya su. Ya ce, idan babu ci gaban Afrika, ba za a samu wadata a kasashen duniya ba. Ya kamata kasashen duniya su taimakawa kasashen Afrika. Ya ci gaba da bayyana cewa, kasar Sin ta zama daya daga cikin kasashen da suke taimakawa kasashen Afrika a farko, kuma irin taimakon da Sin ta bayar, sun kasance masu amfani, kuma kasashen duniya sun amince da wannan. Dalilin da ya sa hadin gwiwar da ke tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika zai iya haifar da babban tasiri shi ne, yayin da Sin take raya hakikanin hadin gwiwa da kasashen Afrika, kullum ta kan nace wajen bin hanyar cikin daidaito da rike amana, da bisa sahihiyar zuciya. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China