in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babbar manufar kasar Sin a fuskar diplomasiyya ita ce nuna adalci, in ji ministan kasar
2014-01-11 16:33:54 cri
Ministan kasar Sin mai kula da harkokin waje, mista Wang Yi, ya bayyana a ranar Jumma'a 10 ga wata, a kasar Senegal, cewa babbar manufar kasar Sin ta fuskar diplomasiyya ita ce kokarin nuna adalci.

Mr Wang ya fadi hakan ne bayan da ya gana da takwaransa na kasar Senegal mista Mankeur Ndiaye, yana mai bayanin cewa Shugaban kasar Sin Xi Jinping ne ya bayyana wannan manufar na kokarin nuna adalci lokacin da ya ziyarci nahiyar Afirka a bara. Yace Ma'anar manufar ita ce, kasar Sin za ta mai da hankali kan nuna adalci a kokarinta na mu'amala da kasashen Afirka, inda za ta yi kokarin kulla abokantaka, da tabbatar da daidaituwa, tare da cika alkawuran da ta dauka, haka zalika za ta yi kokarin kare hakkin kasashen Afirka da taimakawa biyan bukatunsu.

Ban da haka kuma, a cewar mista Wang, manufar ta shafi alkawarin da kasar Sin ta dauka na tabbatar da moriyar juna yayin da take hulda da kasashen nahiyar Afirka, inda kasar Sin za ta magance hanyar da Turawa 'yan mulkin mallaka suka bi ta kokarin kwatan albarkatun kasa daga Afirka don biyan bukatansu kawai.

Maimakon haka yace,kasar Sin za ta yi kokari tare da kawayenta dake Afirka don tabbatar da ci gaba da walwala a bangarorin 2. Ban da haka kuma, yayin da Sin da kasashen Afirka suke hadin kai,kasar Sin za ta kara mai da hankali kan bukatun kasashen Afirka. Kuma idan akwai bukata, za ta iya sadaukarwa da moriyar kanta don tabbatar da nuna adalci ga kasashen Afirka. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China