in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a samar da ayyukan jin kai yadda ya kamata a Sudan ta Kudu, in ji MDD
2014-01-04 17:03:03 cri
Jiya Jumma'a 3 ga wata, Ofishin kula da harkokin ba da taimakon jin kai na MDD ya yi kira da a tabbatar da tsaro a hukumomin ba da taimakon jin kai a kasar Sudan ta Kudu ta yadda za su iya samar da taimakon jin kai ga al'ummomin kasar da rikice-rikice suka shafa.

A wannan rana, jami'in kula da harkokin jin kai na MDD da ke kasar Sudan ta Kudu, ya ba da wata sanarwa inda ya nuna cewa, a halin yanzu, hukumomin ba da taimakon jin kai sun himmatu wajen gudanar da ayyukansu a kasar, inda suka samar da abinci, kayyayakin agaji da kuma ayyukan jinya da dai sauransu, kuma suna karfafa ayyukansu wajen samar da karin ruwa mai tsabta da kuma bayan gida. Don haka, ya kamata bangarorin daban daban da abin ya shafa, su tabbatar da samar da tsaro ga hukumomin ba da taimakon jin kai a kasar Sudan ta Kudu, tare da girmama ayyukansu, da kare ma'aikatansu da kuma kadarorinsu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China