in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka ta yi maraba da tattaunawar kawo karshen rikicin Sudan ta Kudu
2014-01-01 16:35:32 cri
Fadar White House ta kasar Amurka ta yi maraba da cimma yarjejeniyar gudanar da tattaunawar samar da zama lafiya tsakanin gwamnatin kasar Sudan ta Kudu da shugaban 'yan tawayen kasar, ta yadda za a kawo karshen makonni da aka shafe ana zubar da jini a wannan jaririyar kasa.

Kakakin fadar ta White House Caitlin Hayden ce ta bayyana hakan cikin wata sanarwa a ranar Talata, inda ta ce, sassan biyu za su aike da wakilai zuwa Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha, don yin tattaunawa bisa shiga tsakanin kungiyar raya gwamnaticin gabashin Afirka.

Jami'ar ta yi kira ga shugaba Salva Kiir da tsohon mataimakinsa Riek Machar, da su hanzarta daukar matakan da suka dace, don kawo karshen rikicin.

Ta ce, kasar Amurka ta damu matuka da halin da ake ciki a Sudan ta Kudu, ganin yadda fararen hula ke ci gaba tagayyara. Don haka, Amurkan ke ci gaba da kira da tsaigata bude wuta, ta yadda za a daidaita lamarin don a samar da kayayyakin agaji ga fararen hulan da ke matukar bukatar taimako. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China