in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin kasar Sudan ta kudu sun tabbatar da ci gaba da gwabza fada tare da magoya bayan tsohon mataimakin shugaban kasar
2013-12-25 20:34:38 cri
Kakakin sojin kasar sudan ta kudu a ranar laraban nan 25 ga wata ya tabbatar da cewa har yanzu ana gwabza fada tsakanin sojojin gwamnati da na tsohon mataimakin shugaban kasar Riek Machar a garin Malakal babban birnin jihar Upper Nile mai arzikin mai, sannan wassu rahotannin na cewa wannan gari yana hannun magoya bayan Riek ne.

Kakakin Sojin kasar Philip Aguer ya sheda ma kamfanin dillancin labarai ta Xinhua ta wayar tarho daga Juba babban birnin kasar Sudan ta kudu cewa lallai ana cigaba da gwabzawa tsakanin bangarorin biyu amma ba zai iya bada cikakken bayani a kan yanayin da ake ciki ba.

Yayi bayanin cewa ya zuwa wannan lokacin suna jiran sakamako ne daga filin daga game da halin da ake ciki sakamakon fadan da ya barke lokacin da sojojin magoya bayan Machar suka kai hari ga sansanin sojan dake Malakal da niyyar karbe ikon shi.

A wani labarin kuma ance sojojin magoya bayan Machar sun karbe ikon mallakar garin na Malakal wanda anan ne aka fi samun albarkatun mai a kasar.

Kamar yadda jaridar dake da ofishi a kasar Faransa,Sudan Tribune ta bada rahoto ta yanar gizonta ance mazauna garin na Malakal da dama sun tabbatar da cewa mummunan fada ya auku a safiyar ranar talata kuma zuwa yammacin wannan rana sojoji masu biyayya ga tsohon mataimakin shugaban kasar sun karbe ikon wannan gari. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China