in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Sudan ta Kudu ba ta amince da sharadin jam'iyyar adawa ba
2013-12-24 19:26:47 cri
A jiya litinin 23 ga wata, tsohon mataimakin shugaban kasar Sudan ta Kudu Riek Machar ya gabatar da sharadinsa na yin shawarwari da shugaban kasar Salva Kiir Mayardit, inda yake neman gwamnati ta saki magoya bayan sa da aka tsare, amma bukatar ba ta samu amincewar bangaren gwamnati ba.

A wannan rana, mista Riek Machar ya bayyana cewa, ya amince da yin shawarwari da shugaba Kiir, amma kafin hakan, wajibi ne a saki magoya bayan sa a fannin siyasa. Ya ce, wadannan magoya bayan nashi su ne za su kasance muhimman membobin kungiyar da za ta yi shawarwari da gwamnatin kasar.

Daga bisani, ministan watsa labaru na kasar, Michael Makuei Lueth ya mai da martani cewa, ba za a biya bukatun Mr Machar ba sannan Gwamnatin kasar za ta yi shawarwari da shi ba tare da wani sharadi ba.

Tun da farko a wannan rana, babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya yi kira ga kwamitin sulhu na MDD da ta kara tura sojojin kiyaye zaman lafiya 5500 a Sudan ta Kudu, don tallafawa sojojin majalisar kimanin 7000 dake kokarin kiyaye zaman lafiya a kasar a halin yanzu, ta yadda za a samu damar tinkarar barazanar yanayin tsaro da kuma ba da kariya ga fararen hula da ma'aikatan MDD a kasar. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China