in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Cote d'I voire za ta koyi irin masarorin da Sin ta samu a fannin harkokin kiwon lafiya
2013-08-20 20:40:12 cri
Ministan harkokin kiwon lafiya na kasar Cote d'Ivoire Raymonde Goudou-dou-Coffie, ya bayar da misali da yadda kasar Sin ta ke amfanin da tsarin magungunan gargajiya dana zamani a lokaci guda a matsayin tsarin da ya kamata Afirka ta yi koyi da shi, musamman kasar Cote d'Ivoire.

Ministan ya bayyana hakan ne a ranar Litinin, bayan kammala ziyarar kwanaki 3 da ya kawo zuwa kasar Sin, inda ya ce nasarar da kasar Sin ta samu wajen amfani da magungunan gargajiya dana zamani a cibiyoyin kiwon lafiya,shi ne tsarin da ya kamata a yi koyi da shi.

Ministan ya zo kasar Sin ne karkashin laimar dandalin ministocin kiwon lafiya na kasashen Sin da Afirka,wanda aka kafa da nufin bunkasa hadin gwiwa a bangaren kiwon lafiya, da gano sassan da bangarorin biyu suke dora muhimmanci.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China