in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jirgin ruwan soja na Sin ya kama hanyar tekun Mediterranean
2014-01-01 20:15:42 cri
Kakakin rundunar sojojin tekun kasar Sin Liang Yang ya bayyana a Talata 31 ga watan Disamba na shekarar 2013 cewa, jirgin ruwan soja na kasar Sin ya riga ya kama hanyar zuwa tekun Mediterranean, don kare jiragen ruwan da ke jigilar makamai masu guba na kasar Syria.

Bayan da wannan jirgin ruwan sojan kasar Sin ya isa tashar jiragen ruwa na Limassol dake kasar Cyprus, zai hadu da jiragen ruwan soja na sauran kasashe, sa'an nan kuma za su fara ayyukansu, a kokarin da ake yi na lalata makamai masu guba na kasar Syria. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China