in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ba ta amince da sharuddan da aka gindaya na taron Geneva karo na 2 ba
2013-11-12 20:13:17 cri
Kasar Sin a ranar Talata 12 ga wata ta yi kira ga dukkan bangarorin da abin ya shafa da su halarci taron Geneva karo na 2 ba tare da wani sharadi ba domin kawo karshen rikicin kasar Syria.

Qin Gang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin wanda ya furta hakan wajen taron manema labarai ya ce, kin amincewar hakan ya biyo bayan sharuddan da kungiyar adawa ta kasar Syria wato SNC ta gindaya kafin ta halarci wannan babban taron sulhu.

Sin, in ji shi, a kullum ta yi imani cewa, ta hanyar siyasa ne kadai za'a iya bi a sulhunta wannan matsalar ta Syria, wanda kuma sauran kasashen duniya ma suka lura da hakan.

Qin Gang ya yi bayanin cewa, yana da matukar muhimmanci ga dukkan bangarorin su goyi bayan kokarin wakilin magatakardar MDD Ban Ki-Moon da manzon musamman na kungiyar tarayyar kasashen Larabawa da MDD Lakhdar Brahimi, a kokarin ganin ko wane ya shiga cikin taron Geneva karo na 2 ba tare da wani sharadi ba.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China