in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu ma'aikatan kiyaye zaman lafiya na M.D.D. sun janye daga kasar Sudan ta Kudu
2013-12-23 10:49:27 cri
A ranar 22 ga wata, ofishin kakakin M.D.D. ya ba da wata sanarwa, inda ya bayyana cewa, a wannan rana, an janye wasu mambobin tawagar musamman ta M.D.D. a kasar Sudan ta Kudu, wato UNMISS zuwa kasar Uganda.

A cikin sanarwar, an ce, a wannan rana, an fara kwashe wasu ma'aikatan UNMISS daga birnin Juba, babban binrin kasar Sudan ta Kudu, zuwa birnin Entebbe na kasar Uganda, kuma sauran ma'aikatan UNMISS za su ci gaba da ba da taimako ga fararen hula kimanin dubu 20 da ke neman mafaka a ofishin UNMISS dake birnin Juba. Ban da wannan kuma, a wannan rana kuma, za a kwashe wasu ma'aikatan na MDD daga birnin Bentiu, hedkwatar jihar Unity da ke kasar Sudan ta kudu.

Ban da wannan kuma, sanarwar ta ce, UNMISS za ta ci gaba da yin kokari tare da kasashen duniya da shiyya-shiyya, don lalubo bakin zaren warware batun kasar. Idan al'amura suka inganta a kasar, za a dawo da ma'aikatan da suka janye daga birnin Juba. Ban da wannan kuma, UNMISS ta yi shirin kara jibge sojoji a garuruwan Bor, Bentiu don tabbatar da tsaron jama'a.

A wannan rana da karfe 7, dakarun da ke dauke da makamai kimanin 2000 sun kai hari ga wani sansanin UNMISS da ke birnin Akobo na jihar Jonglei na kasar, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar sojojin kiyaye zaman lafiya 'yan asalin India guda 2 tare da fararen hula a kalla 11. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China