Mr. Zhong ya bayyana cewa, kasashen gabashin Afirka sun yi allah wadai da a mai da rikicin siyasa a matsayin rikicin kabilu da na addinai, a yayin taron koli na kungiyar raya gwamnatocin gabashin Afirka ta IGAD, an yi kira da a tsayar da rikice-rikice a kasar Sudan ta Kudu, kuma a halin yanzu ana damuwa sosai kan rikice-rikicen da watakila za su bazuwa a tsakanin wasu kabilun kasar Sudan ta Kudu.
Mr. Zhong ya kuma kara da cewa, kasar Sin tana son ba da taimako wajen kawo karshen tashen hankulan jama'ar kasar Sudan ta kudu, da kuma ciyar da aikin shimfida zaman karko a kasar Sudan ta kudu gaba. (Maryam)