A wannan rana, 'yan sanda sun yi yunkurin shiga gidan kwana na Ntsourou don gudanar da bincike, abin da ya kawo fada da dakarun da ke goyon bayan Ntsourou kimanin 100, inda aka yi musayar wuta, daga karshe Ntsourou ya mika kansa ga 'yan sanda.
An samu wanzuwar zaman lafiya da doka daga bisani a babban birnin kasar, sannan a wannan rana, 'yan sanda sun ba da sanarwar cewa, wassu dakaru masu dauke da makamai sun kai musu hari a ranar Lahadi 15 ga wata, daga bisani kuma, an gano cewa, akwai alakar tsakanin wadannan dakarun da Ntsourou.
Ana tuhumarsa ne da laifin boye makamai, da kafa dakarunsa, daga bisani kuma, an ba da sammacin bincike inda aka danka wa 'yan sanda iznin binciken gidan Ntsourou.(Bako)