in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan tawayen M23 sun zargi gwamnatin Kinshasa da kawo cikas ga cimma yarjejeniyar samar da zaman lafiya
2013-11-13 17:09:19 cri
A ranar 12 ga wata, kungiyar 'yan tawayen M23 ta bayyana cewa, yadda gwamnatin Kinshasa ta canja ra'ayicanja ra'ayinta ya yi sanadin rashin cimma daddale yarjejeniyar samar da zaman lafiya tsakaninsu a yayin bikin rattaba hannu na ranar 11 ga wata.

Wani babban jami'in 'yan tawayen M23 ya ce, a ranar 4 ga wata, kungiyar M23 da gwamnatin kasar Congo Kinshasa sun cimma matsaya guda game da abubuwan da za a tanada cikin yarjejeniyar samar da zaman lafiya da za su daddale, amma yayin da wakilan gwamnatin kasar suka isa birnin Kanpala hedkwatar kasar Uganda domin daddale wannan yarjejeniya, sun ba da shawarar canja yarjejeniyar zuwa wata sanarwa. '"Yan tawayen M23 sun bayyana cewa, ba za su amince da wannan ba, sabo da bangarorin biyu sun kammala yin shawarwari da shirin daddale yarjejeniya, ciki har da batun kwance damarar 'yan tawayen M23 da sauransu。

Har zuwa yanzu gwamnatin Kongo(Kinshasa) ba ta bada wani karin haske game da matakin data dauka kan wannan batu ba.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China