in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musamman na babban magatakardar M.D.D. ya yi maraba da farfado da shawarwari tsakanin gwamnatin Kongo(kinshasa) da dakaru masu adawa
2013-06-08 15:22:06 cri
A ranar 7 ga wata, manzon musamman na babban sakataren M.D.D. game da batun yankin babban tafki na Afrika kuma tsohuwar shugabar kasar Ireland Mary Robinson, ta ba da wata sanarwa, inda ta yi maraba da farfado da shawarwari tsakanin gwamnatin Kongo(kinshasa) da dakarun 'yan tawayen kasar wato M 23 wanda za a yi a birnin Kampala babban birnin kasar Uganda.

A cikin sanarwar, Robinson ta bukaci gwamnatin Kongo(kinshasa) da dakarun adawa na M23, da su yi shawarwari cikin tsanaki, don warware matsalolin da ke tsakaninsu, da ingiza farfado da halin da ake ciki a yankunan gabashin kasar. Ta jaddada cewa, cimma burin samar da zaman lafiya da karko ta hanyar siyasa, na da ma'anar musamman game da jama'ar kasar Kongo(kinshasa).

A watan Afrilu na shekarar 2012, dakarun kungiyar NCDP ta kasar Kongo(kinshasa) ta ta da bore, inda suka kafa dakarun adawa da gwamnatin kasar mai suna M23, kuma a watan Nuwambar bara, sun mamaye birnin Goma da ke lardin Nord-Kivu a yankin gabashin kasar. A ranar 7 ga watan Disamba na bara, gwamnatin Kongo(kinshasa) da dakarun M23, sun fara yin shawarwari a birnin Kampala, amma har yanzu, kwalliya ba ta biya kudin sabulu ba.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China