in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala aikin jibge rukunin sojojin kiyaye zaman lafiya na Sin a Mali zagaye na farko
2013-12-13 20:28:40 cri
A safiyar ranar Alhamis 12 ga wata, aka kammala aikin jibge rukunin sojoji 135 na kiyaye zaman lafiya na Sin a Mali zagaye na farko, tare da yin atisayen soja a karo na farko. Kafin wannan, an riga an isar da kayayyaki da nauyinsu ya kai sama da ton 1700 a sansanin su ta jirgin ruwa.

Ofishin kula da harkokin kiyaye zaman lafiya na ma'aikatar tsaron kasar Sin ya bayyana cewa, bayan isowarsu a yankin Gao na Mali, sojojin kiyaye zaman lafiya na Sin sun fara daidaito kan yanayin tsaro da kuma yanayi mai zafi sosai a can, tare da shirya tantuna da kafa shingayen kariya. Yanzu sun riga sun kammala shiri don karbar duk ayyukan da za a basu.

Baki daya rundunar sojan kiyaye zaman lafiya ta Sin a Mali zagaye na farko ta hada da sojoji 395, wadanda aka kebe su zuwa rukunin sojojin injiniyoyi, da na ba da jiyya, da na yin rangadi. Yanzu sauran sojojin kasar Sin su ma sun kammala shirinsu domin a girke su a Malin, kuma za su iya tashi bisa lokacin da MDD ta sanar.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China