in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojan kiyaye zaman lafiya a Mali ta Sin ta kafu a karo na farko
2013-07-12 20:32:32 cri
A ranar Jumma'a 12 ga wata, an yi bikin kafa rundunar sojan kiyaye zaman lafiya a Mali ta kasar Sin a birnin Harbin, abin da ya zame karo na farko da Sin za ta tura rundunar soja na kwantar da tarzoma domin kiyaye zaman lafiya a kasashen waje.

Wannan rundunar soja ta hada da hafsoshi da sojoji 395, ciki har da wani rukunin injiniyoyi mai kunshe da sojoji 155, da wani rukunin kiyaye tsaro mai kunshe da sojoji 170, da kuma wani rukunin ba da jiyya mai dauke da sojoji 70. Za a kasa wannan rundunar sojan kashi biyu domin tafiya zuwa Mali a karshen watan Yuli da kuma farkon watan Satumba na bana, a kokarin daukar nauyin gyara hanyoyi da gadoji, da kiyaye sansanin soja, da ba da jiyya da sauransu.

Kafin wannan, sun riga sun koyi ka'idojin aikin kiyaye zaman lafiya, da samun horon fasahohin kiyaye zaman lafiya da yaki da ta'addanci da sauransu.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China