in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi tir da barkewar tashin hankali a Arewacin Mali
2013-11-30 16:31:10 cri
Tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD dake Mali wato MINUSMA, ta yi Allah wadai da aukuwar tashin hankali a yankin Kidal dake Arewacin kasar ta Mali, daidai lokacin da Firaministan kasar ke shirin ziyartar yankin a ranar Alhamis.

Rahotanni daga yankin na Kidal sun ce, lamarin ya faru ne sakamakon kokarin da wasu masu zanga-zanga suka yi, na hana firaministan kasar shiga yankin na Kidal, wanda ke hannun 'yan tawayen azbinawa.

A cewar mai magana da yawun MDD Martin Nesirky, tawagar ta MINUSMA na fatan dukkanin sassan da wannan lamari ya shafa za su kai zuciya nesa, su kuma martaba yarjeniyoyin wanzar da zaman lafiya da aka kulla a baya.

Dauki ba dadin da sojojin gwamnati suka yi da masu zanga-zanga a Kidal din dai, ya sabbaba jikkatar mutane da yawa, ko da yake ba a tabbatar da yawan mutanen da suka rasa rayukansu ba.

Mahukuntan kasar Mali dai na yunkurin farfado da yanayin zaman lafiya, da tabbatar da mulkin dimokaradiyya a kasar, bayan shafe shekaru ana dauki ba dadi da 'yan tawaye masu alaka da kungiyar Al-Qaida, wadanda suka kwace ikon yankin Arewacin kasar. Daga bisani aka kulla yarjejeniyar tsagaita wuta bayan tsoma bakin wasu kasashen duniya, da kwamitin tsaron MDD.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China