in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rukunin farko na tawagar sojojin kiyaye zaman lafiya na kasar Sin ya shirya tashi zuwa kasar Mali
2013-11-18 21:08:23 cri
Rukunin farko na tawagar sojojin kiyaye zaman lafiya na kasar Sin da zai je kasar Mali ya shirya sosai don zuwa wurin da zai yi aiki bisa shirin MDD a ko wane lokaci.

A ranar 25 ga watan Afrilu na bana ne, kwamitin sulhu na MDD ya zartas da wani kuduri, inda aka kafa tawagar hadin gwiwa ta kiyaye zaman lafiya a kasar Mali. Bisa bukatun MDD, kasar Sin ta tsaida kudurin tura tawagar sojojin kiyaye zaman lafiya dake kunshe da sojoji masu aikin gine-gine, kiwon lafiya da kuma kiyaye tsaro guda 395 zuwa wuraren da za su yi aiki. Wannan ne karo na farko da kasar Sin ta tura sojojin tsaro da za su shiga aikin kiyaye zaman lafiya na MDD. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China