in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kada kuri'u a zagaye na farko a zaben majalisar dokokin kasar Mali
2013-11-25 10:05:39 cri

A ranar 24 ga wata ne, aka fara kada kuri'u a zagayen farko na zaben majalisar dokoki na kasar Mali, inda masu zabe za su zabi 'yan majalisun dokoki 147 daga cikin 'yan takara 1082.

Bisa shirin da aka yi, an ce, za a fara jefa kuri'a a ranar 24 ga wata da karfe 8 na safe, kuma za a kammala shi a ranar 18 ga wata. Bisa labarin da aka samu, an ce, masu zabe da yawansu ya kai sama da miliyan 6.5 ne za su kada kuri'u a zaben, kuma 'yan takara karkashin jam'iyyu da 'yan takara masu zaman kansu ne za su shiga zaben a gundumomi 55 na kasar.

Majalisar dokokin kasar Mali ita ce hukuma mafi girma ta kasar Mali, kuma 'yan majalisun da aka zaba, za su yi wa'adin tsawon shekaru 5. Za a gudanar da zagaye na biyu na zaben majalisar dokokin kasar a ranar 15 ga watan Disamba. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China