in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatar ilimi ta Najeriya ta kaddamar da wasu hukumomin ilimi a kasar
2013-10-29 15:21:00 cri


Ranar Litinin 28 ga wata ne, ma'aikatar ilimi ta tarayyar Najeriya ta kira wani babban taro a hukumar kula da harkokin jami'o'i ta kasar wato NUC dake Abuja, babban birnin tarayya, inda aka kaddamar da wasu muhimman sassan ilimi na kasa. Wakilinmu Murtala dauke da karin bayani.

Taron da ya samu halartar manyan shugabanni, jami'ai da masana a fagen ilimi na Najeriya, an yi shi ne a babban dakin taro na hukumar kula da jami'o'i ta kasa wato NUC dake birnin Abuja. Ministan ilimi na Najeriya cif Ezenwo Nyesom Wike, da shugaban hukumar NUC Dr. Ahmadu Ali, da Alhaji Aminu Suleiman wanda shi ne shugaban kwamitin kula da harkokin ilimi na majalisar dokokin Najeriya da dai sauran wasu manyan jami'ai ne suka halarci taron.

Daga cikin sassan ilimin da aka kaddamar a wannan karo, akwai majalisar hukumar jami'o'in kasa dake Abuja, da hukumar kula da ilimin kimiyya da fasaha dake jihar Kaduna, da majalisar kula da rajistar malaman koyarwa ta Najeriya dake Abuja, da kauyen koyon harshen Faransanci dake jihar Lagos, wato Nigeria French Language Village a turance, da kuma cibiyar koyon harsunan Najeriya dake jihar Abia. Sauran hukumomin ilimin da aka kaddamar sun hada da makarantu na musamman dake jihohin Niger, Kebbi, Taraba, Jigawa, Anambra, Bayelsa da Zamfara da sauransu.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China