Mista Jacob Zuma wanda yake bakin ciki da alhinin wannan rashi ya bayyana cewa, Mandela ya sadaukar da rayuwarsa wajen yakin neman 'yancin al'umma, wanda hakan ya sa ya samu girmamawa daga dukkanin sassan wannan duniya. Tawali'u da halayyar kaunar jama'a, da kuma ra'ayin jin kai da yake da su sun samu yabo daga jama'a.