in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a karfafa dangantakar girmama juna da cimma moriyar juna tsakanin Sin da Amurka, in ji mataimakin shugaban Sin
2013-12-04 20:28:04 cri

Yau Talata 4 ga wata ne, mataimakin shugaban kasar Sin Li Yuanchao ya gana da takwaransa na kasar Amurka Joseph Biden a nan birnin Beijing.

Yayin ganawarsu, Mr. Li Yuanchao ya bayyana cewa, a watan Yuni na wannan shekarar ce, shugabannin kasashen Sin da Amurka suka cimma ra'ayi daya kan kafa sabuwar dangantakar girmama juna da kuma cimma moriyar juna tsakanin kasashen biyu bisa fannoni daban daban. Kasar Sin tana fatan kara yin mu'amala da kasar Amurka, mutunta juna da kare manyan moriyar kasashen biyu, ta yadda za a karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu yadda ya kamata daga dukkan fannoni, karfafa mu'amalarsu kan harkokin kasashen biyu, shiyya-shiyya da kuma kasa da kasa, don shimfida aniyar girmama juna da kuma cimma moriyar juna cikin harkoki daban daban dake shafar gina dangantakar kasashen biyu.

A nasa bangare, Mr. Biden ya ce, dangantakar dake tsakanin kasashen Sin da Amurka na da muhimmiyar ma'ana ga kasashen duniya. Kasarsa na dukufa wajen karfafa mu'amalar dake tsakanin shugabannin kasashen biyu, bunkasa hadin gwiwar kasashen biyu da kuma warware bambance-bambance dake tsakanin Sin da Amurka yadda ya kamata ba tare da boye kome ba, a kokarin inganta sabuwar dangantaka tsakanin kasashen biyu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China