in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bai kamata hukumomin kasar Amurka su zargi sauran kasashen duniya game da lamarin kai hari a kan internet ba
2013-11-07 20:22:59 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin Hong Lei ya bayyana a yau Alhamis 7 ga wata a gun taron manema labaru cewa, kasar Sin tana fuskantar harin da ake kai mata a kan internet, kuma gwamnatin kasar Sin na nuna adawa ga wannan hari. Ganin yadda ake samu lamarin sa ido kan wayoyi da sakwanin jama'a a kasar Amurka, bai kamata kasar Amurka ta kyale lamarin, amma ta zargi sauran kasashen duniya a wannan fanni ba.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, kwamitin kula da tattalin arziki da tsaro na kasashen Amurka da Sin dake kasar Amurka ya gabatar da wani rahoto ga majalisar dokokin kasar a ranar 6 ga wata, inda ya bayyana cewa, babu alama da ke shaida cewa bangaren soja na kasar Sin ya daina kai hari ga internet ba.

Game da wannan batu, Hong Lei ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Sin na nuna adawa ga kai hari a kan internet, da yin kira ga kasa da kasa da su yi hadin gwiwa da gina yanayin internet mai zaman lafiya, tsaro, bude kofa da kuma hadin gwiwa. A lokacin da bullowar lamarin PRISM sa ido ga bayanan jama'a a kasar Amurka, idan har hukumomin kasar Amurka da abin ya shafa suna sha'awar cimma nasarar batun tsaron internet, sannan bai kamata kasar Amurka ta kyale lamarin, kuma ta fadi lamari na daban ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China