in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijar da Mauritaniya za su yi hadin gwiwa wajen yaki da rashin tsaro a yankin Sahel
2013-12-03 10:36:59 cri
Shugaban kasar Nijar Mahamadou Issoufou da takwaransa na kasar Mauritaniya Mohamed Ould Abdel Aziz dake ziyarar aiki a kasar Nijar sun jaddada niyyar ta hada karfi da karfi domin yaki da ta'adanci da masu fataucin miyagun kwayoyi a yankin Sahel, a yayin wani zaman taron tawagogin kasashen biyu, a cewar kamfanin dillancin labarai na kasar Nijar ANP a ranar Litinin.

Shugaban kasar Nijar ya nuna cewa, bisa ga misalin rikicin kasar Mali, yana da muhimmanci mu maida hankali sosai game da babban hadarin ta'adanci da safarar miyagun kwayoyi da ka iya afkawa kasashen shiyyarmu.

Yarjejeniyar sojoji dake tsakanin kasashe wani muhimmin mataki ne dake bisa hanyar habaka dangantaka mai karfi a wannan fanni, in ji shugaba Mahamadou Issoufou.

A nasa bagare, shugaban kasar Mauritaniya ya jaddada cewa, babbar barazanar da ake fuskanta yanzu ita ce daidaituwar zaman al'umma a wannan sabon karni. Idan ka yi la'akari matsalarmu ita ce tsattsauran ra'ayi yana janyo ta'adanci, in ji mista Abdel Aziz.

Kuma ya bayyana wajabcin kasar Nijar da kasar Mauritaniya da ma sauran kasashen dake wannan shiyya da su yi aiki tare wajen yaki da ta'adanci. Cikin hadin gwiwa ne kawai kasashen yankin Sahel za su gudanar da aiki yadda ya kamata kan kalubalolin dake gabansu wanda muhimmin aiki shi ne tsaro, in ji shugaban kasar Mauritaniya da ya isa birnin Yamai a cikin wata ziyarar aiki ta kwanaki biyu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China