in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban magatakardan MDD ya kammala rangadi a yankin Sahel
2013-11-09 17:10:05 cri
Babban magatakardan MDD Ban Ki-Moon, ya gana da shugaba Idriss Deby na kasar Chadi, a daidai lokacin da yake karkare rangadinsa a kasashen dake yankin Sahel. Yayin ganawar tasu, Ban Ki-moon ya bayyanawa shugaba Deby irin kalubale, da kuma ci gaban da yankin na Sahel ke samu ta fuskar tsaro, da ma alakar hakan da ragowar yankunan dake nahiyar Afirka.

Da yake karin haske ga manema labaru don gane da wannan ziyara, kakakin babban magatakardan MDDr Farhan Haq, ya ce jagororin Biyu sun yi musayar ra'ayi kan halin da ake ciki don gane da batun tsaro, da ayyukan jin kai a kasar Afirka ta tsakiya, suna masu bayyana bukatar karin kulawar kasashen duniya, don gane da halin da ake ciki a kasar. Haka zalika, Mr. Ban ya jaddada muhimmancin hadin gwiwar dukkanin yankuna, da sassan masu ruwa da tsaki na kasa da kasa, a kokarin da ake yi na tinkarar kalubalen dake ci gaba da fuskantar wannan yanki na Sahel. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China