in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar gidajen zama ta Afirka ta ba da rancen kudi dallar Amurka miliyan 10 ga bankin raya kasar Rwanda
2013-12-01 17:18:32 cri
Bisa labarin da aka samu daga kamfanonin dillanci labaran kasar Rwanda, an ce, kungiyar gidajen zama ta nahiyar Afirka za ta ba da rancen kudi na dallar Amurka miliyan 10 ga bankin raya kasa ta Rwanda, don ba da rancen kudi ga iyalan da ba su da isassun kudaden shiga wajen sayan gidajen zama.

Shugaban bankin raya kasa ta Rwanda Alex Kanyankole ya bayyana cewa, rancen kudin da kungiyar ta baiwa bankin zai ba da taimako ga kasar Rwanda wajen biyan bukatun iyalan da ba su da isassun kudin shiga don sayan gidajen zama, da kuma ba da taimako a fannin samar da karin kudade wajen gina gidajen zama masu araha, sakamakon hakan, dukkan al'ummomin kasar Rwanda za su iya samu gidajen zama a karshe.

Bugu da kari, bisa hasashen da bankin raya kasa ta Rwanda ya yi, an ce, rancen kudi na dallar Amurka miliyan 10 da kungiyar gidajen zama ta nahiyar Afirka za ta baiwa bankin, a kalla zai ba da taimako ga iyalai kimanin dubu daya wajen saya a karon farko gidajen zama nasu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China