in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rufe taron tattauanwa na hadin gwiwar Sin da Afirka karo na hudu a birnin Hainan na Sin
2013-11-21 20:34:06 cri
Yau Alhamis 21 ga wata ne aka kammala taron tattaunawa na hadin gwiwar Sin da Afirka karo na hudu a lardin Hainan na kasar Sin. An ba da wata sanarwa a yayin taron, inda ta nuna cewa, taron tattauanwa na hadin gwiwar Sin da Afirka ya kasance wani dandalin musayar ra'ayoyi tsakanin jama'ar Sin da Afirka, tare da ba da dama wajen inganta hadin gwiwar dake tsakanin kamfanonin Sin da Afirka.

An yi taron dandalin tattaunawa tsakanin shugabannin kamfanonin Sin da Afirka da kuma taron tattaunawa kan hadin gwiwar ayyukan noma tsakanin Sin da Afirka, bisa babban taken taro na wannan karo, watau "hadin gwiwa da cimma moriyar juna".

A yayin taron, jami'an ma'aikatar harkokin ayyukan noma ta kasar Sin, masanan ayyukan noma na Sin, jami'an kasashen Afirka da kuma jakadun Afirka dake kasar Sin sun cimma ra'ayi daya cewa, ta hanyar yin hadin gwiwa kan ayyukan noma, Sin za ta iya koyar da kasashen Afirka fasahohin ayyukan noma na zamani ta yadda za ta ba da taimako gare su wajen warware matsalar karancin abinci. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China