in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sada zumunta a tsakanin Sin da kasashen Afirka ya dace da bukatun jama'arsu
2013-06-27 16:38:52 cri
A gun taron tattaunawa a tsakanin magadan biranen kasar Sin da na kasashen Afirka da aka gudanar a birnin Ji'nan dake kasar Sin a ranar 27 ga wata, shugaban hukumar kula da harkokin sada zumunta a tsakanin Sin da Afirka Abdulaidi Amudurexiti ya bayyana cewa, yanzu ana shiga sabon lokaci wajen raya dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka, kana sada zumunta tsakaninsu ya dace da bukatun jama'arsu.

A matsayin aiki daya bayan taron tattaunawa kan hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka, taron tattaunawa a tsakanin magadan biranen Sin da na kasashen Afirka ya kasance wani muhimmin aiki wajen raya sabuwar dangantakar abokantaka ta hadin gwiwa a tsakaninsu.

Tsohon shugaban kwamitin kungiyar AU Jean Ping ya halarci bikin bude taron tattaunawar, kana kungiyar kula da harkokin sada zumunta a tsakanin jama'ar Sin da ta kasashen waje ta ba shi lambar yabo ta manzon sada zumunta na jama'a. A cikin jawabinsa, Jean Ping ya nuna cewa, tsarin samun bunkasuwa na kasar Sin abin al'ajabi ne, kuma kasashen Afirka suna son kara yin hadin gwiwa tare da kasar Sin a dukkan fannoni. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China