in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta aike da wata tawaga zuwa taron shawarwari kan batun nukiliyar Iran na zagaye mai zuwa
2013-11-05 21:15:56 cri
Ran 5 ga wata da yamma, yayin taron manema labaran da aka yi a nan birnin Beijing, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei ya bayyana cewa, kasar Sin za ta halarci taron shawarwari tsakanin kasashe shida da ke batun nukiliyar kasar Iran ya shafa da kuma kasar Iran na zagaye mai zuwa.

Ya bayyana cewa, a halin yanzu, kasar Sin na fatan za a iya yin shawarwari yadda ya kamata bisa ka'idar girmamawa juna da kuma daukar matakan da za su dace don ciyar da harkokin shawarwari gaba, ta yadda za a iya samar da damar da ta dace dangane da warware matsalar nukiliyar kasar Iran yadda ya kamata, daga dukkan fannoni kuma cikin dogon lokaci.

Bugu da kari, bisa labarin da aka samu, an ce, za a gudanar da taron shawarwari kan batun nukiliyar kasar Iran na sabon zagaye a ranar 7 ga watan da muke ciki a birnin Geneva, kuma kasar Sin za ta aike da wata tawaga zuwa taron karkashin jagorancin shugaban sashen kula da harkokin kayyade makamai na ma'aikatar harkokin wajen kasar ta Sin Pang Sen. (Maryam Yang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China