in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a ci gaba da tattaunawa tsakanin hukumar nukiliya ta MDD da Iran
2013-10-29 09:48:07 cri

Hukumar kula da harkokin nukiliya ta MDD ta bayyana cewa, za a ci gaba da tattaunawa tsakanin hukumar da kasar Iran a kwana na biyu ranar Talata 29 ga wata, game da shirin kasar na nukiliya da ake takaddama a kai.

Hukumar kula da makamashin nulkiya ta duniya IAEA ta bayyana cewa, ana sa ran shugaban hukumar Yukiya Amano zai bayar da sanarwa bayan tattaunawar ta ranar Talata tsakanin sassan biyu.

A ranar Litinin ne aka fara wannan tattaunawa tsakanin bangarorin biyu, game da batun yadda za a nazarci muhimman takardu na cibiyoyin nukiliyar kasar, bayan ganawa tsakanin mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi da Mr. Amano.

A baya dai, hukumar ta IAEA ta yi ganawa sau 12 da Iran tun a shekara ta 2011, amma babu wani tudun dafawa da aka cimma game da duba cibiyoyi da baki dayan shirin nukiliyar kasar ta Iran. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China