in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta ci gaba da taka rawa wajen sa kaimi kan warware batun nukiliyar Iran cikin lumana
2013-10-30 18:49:00 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana a ranar Laraba 30 ga wata a nan Beijing cewa, kasar Sin ta yi maraba da bullowar kyakkyawar alama kan batun nukiliyar kasar Iran sakamakon kokarin da Iran da bangarori masu ruwa da tsaki suke yi tare. Kasar Sin za ta kuma ci gaba da taka rawa wajen sa kaimi kan warware batun cikin lumana bisa tsarin yin shawarwari tsakanin kasashe 6.

Shugaba Xi ya yi wannan bayani ne a yayin da yake ganawa da Ali Larijani, shugaban majalisar dokokin kasar Iran da ke ziyara a kasar Sin a wannan rana. Ya kara da cewa, kasar Sin a tsaye take kan daidaita hulda a tsakaninta da Iran bisa manyan tsare-tsare da hangen nesa, tana son gama kai da Iran wajen ci gaba da inganta zumuncin gargajiya da ke tsakanin kasashen 2, da kara azama kan bunkasuwar dangantakar abokantaka da hadin gwiwa a tsakaninsu a fannoni daban daban yadda ya kamata.

A nasa bangaren kuma, Larijani ya ce, kasarsa ta Iran na dora muhimmanci kan raya hulda a tsakaninta da kasar Sin, tana sa ran inganta mu'amala da hadin gwiwa tare da Sin a fannonin tattalin arziki da cinikayya, makamashi, zuba jari da dai sauransu. Kana kuma Larijani ya yi wa mista Xi bayani dangane da ra'ayin Iran kan batun nukiliyar da kuma halin da ake ciki a shiyya-shiyya.(Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China