in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNEP ta yaba wa kasar Sin kan kokarin da take yi na neman dauwamammen ci gaba
2013-10-29 15:50:39 cri
A ranar 28 ga wata, an bude taron baje kolin ci gaban kasashe masu tasowa karo na shida a Nairobi, babban birnin kasar Kenya. A yayin taron mataimakin babban sakataren MDD, kuma shugaban hukumar kiyaye muhalli ta MDD wato UNEP Achim Steine ya nuna yabo ga kasar Sin kan kokarin da take yi na neman dauwamammen ci gaba.

Mr. Steine ya ce, kasar Sin na mai da hankali sosai kan kiyaye muhallin halittu, ta kuma sa kaimi ga kamfanoni masu zaman kansu da su ci gaba da rage fitar da abubuwa masu gurbata muhalli yayin da suke gudanar da ayyukansu. Matakan da kasar Sin ta dauka sun nuna kokarinta wajen neman daidaito tsakanin bunkasa tattalin arziki da kuma kiyaye muhalli, sannan kuma za ta ci gaba da haka a nan gaba. Lamarin ya zama wata babbar dama ga kasashe masu neman daidaito tsakanin kiyaye muhalli da neman bunkasuwa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China