in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Lakhdar Brahimi ya kai ziyara Syria don shirya taron Geneva karo na biyu
2013-10-29 10:54:22 cri
Ranar Litinin 28 ga wata ne, wakilin musamman na MDD da kungiyar tarayyar kasashen Larabawa game da warware matsalar Syria Lakhdar Brahimi ya isa Damascus, babban birnin kasar, don shirya taron Geneva karo na biyu.

Bisa labarin da aka samu, an ce, cikin 'yan kwanaki masu zuwa, Mr. Brahimi zai gana da shugaba Bashar al-Assad da sauran manyan jami'an gwamnatin kasar da kuma wakilan 'yan adawar kasar. Kuma ana saran yayin ganawarsa da wakilan 'yan adawa, zai ba da shawara ga 'yan adawa ta cikin gida da wadanda ke ketare da su kafa wata tawagar hadin gwiwa don halartar taron na Geneva karo na biyu inda za a tattaunawa kan yadda za a warware matsalar kasar ta Syria. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China