in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar OPCW ta binciki kan wuraren tanadar makamai masu guba 18 a kasar Siriya
2013-10-24 10:54:12 cri
A ranar 23 ga wata, a birnin Hague da ke kasar Holland, cibiyar kungiyar hana yaduwar makamai masu guba ta duniya wato OPCW, an yi taron manema labaru, inda aka bayyana sabon ci gaba da kungiyar ta samu wajen lalata makamai masu guba a kasar Siriya, tare da bayyana cewa, an gudanar da ayyukan lalata makamai masu guba yadda ya kamata, sannan kuma ta gamsu game da hadin gwiwa da kasar Siriya ta bata.

Kakakin kungiyar OPCW Michael Luhan ya ce, ya zuwa ranar 22 ga wata, kwararru na kungiyar sun yi bincike a wuraren tanadar makamai masu guba 18 daga cikin dukkansu 23 a kasar Siriya, sannan aka rufe duk muhimman nau'rori a wadannan wurare. Luhan ya ce, ana gudanar da aikin lalata makamai masu guba bisa shirin da aka tsara, bayan ranar 1 ga watan Nuwamba, Siriya ba za ta iya kera makamai masu guba ba. Kungiyar OPCW tana da kwararru 27 a kasar Siriya, sannan akwai guda da yake kasar Lebanon.

Haka kuma, inji kakakin kungiyar an kafa rukunonin kwararru guda 3 don su iya gudanar da aikinsu, ya zuwa yanzu, an gudanar da aiki yadda ya kamata. Amma, kwararru na kungiyar ba su je yankunan da bangaren 'yan adawa ke mamaye ba don gudanar da bincike ba.

Michael Luhan ya ce, an samu hadin gwiwa tsakanin kungiyar da M.D.D. yadda ya kamata, kuma kasar Siriya ita ma tana bada hadin gwiwa yadda ya kamata. Bisa shawarar da kungiyar OPCW ta yanke a ranar 27 ga watan Satumba, kasar Siriya za ta mika shirin lalata makamai masu guba na farko ga kungiyar OPCW kafin ranar 27 ga watan Oktoba.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China