in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nahiyar Afirka ta kasance sabon zangon fataucin miyagun kwayoyi
2013-10-18 16:36:33 cri
Bisa labarin da aka samu daga kamfanin dillacin labarai na Xinhua ran 17 ga wata, an ce, tun daga ranar 15 zuwa 17 ga wata, yayin taron yaki da laifuffukan da suka shafi miyagun kwayoyi na yankin, jami'an yaki da masu fataucin miyagun kwayoyi na kasashen Afirka da dama sun bayyana cewa, nahiyar Afirka ta riga ta kasance wani sabon zangon fataucin miyagun kwayoyi na kasa da kasa, bugu da kari, babbar matsalar da ake fuskanta ita ce, masu fataucin miyagun kwayoyi sun hada kai da 'yan ta'adda a yankin.

An gudanar da taron ne a Harare, babban birnin kasar Zimbabwe, Jami'in kula da harkokin zamantakewar al'umma na kungiyar tarayyar kasashen Afirka ya bayyana cewa, cikin 'yan shekarun da suka gabata, an samu karuwar laifuffuka da ke da nasaba da miyagun kwayoyi a kasashen Somaliya, Kenya da kuma Tanzania.

Manyan dalilan da ya sa kungiyoyin da ke fataucin miyagun kwayoyi na kasa da kasa ke gudanar da ayyukansu a nahiyar su ne, gurbin da nahiyar take, da rashin aiwatar da dokoki dangane da haramta fataucin miyagun kwayoyi, Kana abin da ya fi tada hankulan jama'a shi ne, a halin yanzu masu fataucin miyagun kwayoyi sun hada kai da 'yan ta'adda, kamar a arewacin kasar Mali, kungiyoyi masu tsattsauran ra'ayi sun tattara kudi ta hanyar fataucin miyagun kwayoyi inda suka goyi bayan harin ta'addancin da suka kai.

Jami'in ya kuma bayyana cewa, ya kamata kasashen Afirka su karfafa hadin gwiwa tsakaninsu da kuma yin musayar ra'ayoyi don yaki da lafuffukan da suka shafi miyakun kwayoyi. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China