in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi kira ga kasa da kasa da su dauki nauyi wajen yaki da miyagun kwayoyi
2011-06-27 14:20:49 cri

Ranar 26 ga watan Yuni ranar yaki da miyagun kwayoyi ta duniya ce. A wannan rana, babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya yi kira ga gwamnatocin kasa da kasa da su dauki nauyi wajen yaki da sumogar miyagun kwayoyi, kamata ya yi bangarori daban daban na zamantakewar al'ummomin kasa da kasa su dauki alhakin sa jama'ar kasar su yi yaki da miyagun kwayoyi.

Ban Ki-moon ya bayyana cewa, sumogar miyagun kwayoyi ta kawo barazana ga lafiyar jama'a da zaman lafiyar yankuna. Kasuwar sayar da miyagun kwayoyi ta kasar Afghanistan da take samun ribar dala biliyan 61 a kowace shekara tana samar da kudi ga masu tada zauna tsaye da 'yan ta'adda na duniya. Kana a yankin yammacin Afirka, cinikin hodar iblis a duniya ya kawo illa ga harkokin siyasa da zaman lafiya a kasashen yankin.

Ban da wannan kuma, Ban Ki-moon ya ce, MDD ta kafa wani rukuni don tsara manufofi a kokarin kyautata hanyoyin yaki da miyagun kwayoyi da aikata miyagun laifuffuka a sakamakon shan miyagun kwayoyi.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China