in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar yaki da miyagun kwayoyi ta kama mutane 114 a jihar dake arewacin Nigeriya
2012-12-23 16:09:11 cri
Hukumar yaki da shan miyagun kwayoyi a Nigeriya NDLEA ta ce, tsakanin watan Janairun bana zuwa Decemban da muke ciki, hukumar a jihar Niger dake arewacin kasar ta kama wadanda ake zargi da sha ko safara da mallakan kilo 517.2 na miyagun kwayoyi da suka hada da wiwi da sauran miyagun kwayoyi masu saka maye.

Shugaban hukumar a jihar Abdullahi Abdul wanda ya sanar da hakan ga manema labarai a Minna, babban birnin jihar a lokacin da yake bayanin nasarorin da hukumar ta samu a cikin wannan shekarar, ya ce, galibin kwayoyin da matasa suke amfani da shi a jihar wiwi ne da sauran kwayoyi masu saka maye.

A cewarsa, tuni mutane 51 tsakanin shekaru 18 zuwa 40 babban kotun gwamnatin tarayya ta yanke masu hukunci. sannan kuma akwai saura da suke jiran hukunci. Ya yi bayanin cewa, a cikin wannan lokacin an gyara rayuwar wassu mashayan su 69 da yanzu haka sun daina shaye shaye tare da komawa cikin 'yan uwansu.

Shugaban hukumar ta NDLEA a jihar Niger Abdullahi Abdul don haka ya yi kira ga iyaye, shugabannin addini da kuma masu fada a ji a cikin al'umma da su taimaka ma hukumar wajen wayar da kan jama'a domin a samu nasarar yaki da shan miyagun kwayoyi.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China