in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD na kira da a dauki matakai kan miyagun kwayoyi da ke fitowa daga Afghanistan
2012-02-17 16:09:00 cri
A jiya Alhamis a birnin Vienna, babban magatakarda na MDD Ban Ki-moon ya yi kira ga hukumomi na kasa da kasa da su dauki mataki guda domin dakatar da shigowa da hodar ibilis da kuma tabar wiwi daga kasar Afghanistan, zuwa kasashen duniya daban-daban. Daukar matakin zai taimaka wajen kawar da bala'in safarar miyagun kwayoyi da kuma amfani da su fiye da kima.

Alkaluman kididdiga sun yi kiyasin cewa, kashi 15 cikin 100 na kudin shiga da kasar ke samu suna shigowa ne ta hanyar safarar miyagun kwayoyi, abun da ke nuna cewa, wannan bangare ya kasance wani bangare mai matsala. Safarar miyagun kwayoyi da aikin ta'addanci kan iyakoki na nakasa karfin dangantaka da zumunci tsakanin kasashe masu rauni, ya na kuma yin karen-tsaye ga dokoki tare da hana cimma muradin karni na MDD ta fannin ci gaba, cewar Ban Ki-moon a lokacin taron ministocin kasashe da suka amince da kudurin garin Paris kan gwagwarmayya da safarar miyagun kwayoyi da ake fitowa da su daga kasar Afghanistan.

Kokowa domin murkushe safarar miyagun kwayoyi shi ne za mu yi bakin kokarinmu, sabili da rage talauci da kuma kara bunkasa rayuwar al'umma, kamar yadda ya furuta a taron garin Vienna na kasar Austriya.(Abdou Halilou)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China