in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar EU tana adawa da warware batun Siriya ta hanyar daukar matakan soji
2013-09-06 16:11:25 cri
A ranar 5 ga wata, a gun taron manema labaru da aka shirya a birnin St. Petersburg na Rasha, shugaban kwamitin zartaswar kungiyar EU Von Rompuy ya bayyana cewa, kungiyar EU tana adawa da warware batun Siriya ta hanyar daukar matakan soji, kuma ya kamata a bayar da sakamakon binciken makamai masu guba da aka zargin an yi amfani da su a kasar ta Siriya tun da wuri.

Von Rompuy ya ce, ya kamata a warware batun Siriya a karkashin inuwar M.D.D., kuma ba zai yiwu a warware batun ta hanyar soji ba, ya ce, hanyar da ta fi dacewa a bi ita ce, siyasa.

A wannan rana, kakakin fadar shugaban kasar Rasha Dmitry Peskov ya sake jaddada cewa, kwamitin sulhu na M.D.D. shi ne kawai zai iya amince da daukar matakan soji a fannin dangantakar kasa da kasa, kuma wasu kasashe da ke zargin Siriya ta yi amfani da makamai masu guba bisa ganin damarsu, ba su dauki matakin da ya dace da huruminsu ba.

A wata sabuwa kuma, a ranar 5 ga wata, kafofin yada labaru na kasar Turkiyya sun bayyana cewa, yanzu, ana ci gaba da jibge sojojin kasar a kan iyakokin da ke tsakaninta da kasar Siriya, don tinkarar kalubale daga kasar ta Siriya. Haka kuma, kwanan baya, shugaban kasar Turkiyya, da firaministan kasar sun bayyana cewa, idan aka tabbatar da gwamnatin Siriya ta yi amfani da makamai masu guba, kasar Turkiyya, za ta goyi bayan daukar matakan soji kan kasar Siriyan.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China