in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bangaren adawa na Siriya ya ci gaba da fatataki sansanin sojojin sama na gwamnati
2013-08-07 15:59:48 cri
A ranar 6 ga wata, dakarun da ke adawa da gwamnatin Siriya mai suna sojojin 'yantar da kasar Siriya sun sanar da cewa, sun mamaye sansanin sojojin sama na Minnigh a lardin Aleppo dake yankin arewacin kasar, to, amma daga bisani sojojin gwamnatin sun musunta wannan labari. A sa'i daya kuma, dakarun dauke da makamai da ke lardin Lattakia a bakin teku na yankin arewacin kasar sun ce, sun kusan isa garin shugaban kasar, Bashir Al-Assad, kuma ana yaki ba kakkautawa a wurare da dama a lardin Lattakia.

Bisa labarin da gidan telebijin na Al-Arabiya da na Al Jazeera suka bayar, an ce, dakarun adawa da gwamnati sun riga sun mamaye sansanin sojojin sama na Minnigh.

A sa'i daya kuma, a ranar 6 ga wata, kamfanin dillancin labaru na Siriya ya ruwaito daga wata majiya cewa, an musunta labarin cewa, bangaren adawa ya mamaye sansanin Minnigh, inda wannan majiya ta ce, sojojin gwamnatin da ke kewaye da sansanin Minnigh sun fafata yaki da 'yan ta'adda, kuma dukkan ma'aikatan da ke sansanin suna cikin koshin lafiya.

A wata sabuwa kuma, kwanan baya, dakarun da ke adawa da gwamnati sun mamaye garin Alawites da ke lardin Lattakia, kuma sun fara isa kusa da garin shugaba Assad wato al-Khalidieh. Gidan telebijin na Al-Arabiya ya ruwaito bayani daga bangaren adawa cewa, yanzu, dakaru masu adawa da gwamnati suna gwabza fada da sojojin gwamnati a garin Alam da ke arewa da al-Khalidieh. A wannan rana kuma, kamfanin dillancin labaru na Siriya ya ba da labari cewa, sojojin gwamnati sun riga sun maido da zaman lafiya da kwanciyar hankali a garin Alam, kuma sun murkushe 'yan ta'adda da ke wurin.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China